.

Brief History of Sardaunan Katsina Ambassador Ahmed Rufai Abubakar, CFR

English Language

Family Background

Amb. Ahmed Rufa’i Abubakar is a descendant of Muhammad Maude, a warrior, and warlord of repute, who established Unguwar Maude in Katsina in the last quarter of the nineteenth century. Muhammad Maude had sixteen children, eight girls and eight boys among whom a set of twins, Hassan and Hussaini the grandfather of Ahmed Rufai Abubakar Sardaunan Katsina. What is today known as Unguwar Maude was Muhammad Maude’s fortress, farmland, and household. Maude was an outstanding warrior famously called Dan Marusa, Mai Wuta. Understandably, he was closely associated with the palace and title holders in the Katsina Emirate. So were some of his children, like Hassan who served in the Katsina Palace as Sarkin Dogarai. So Hassan, the twin brother of Hussaini (the grandfather of Rufai), was part of the traditional ruling elites. Hassan himself never had a child but his brother Hussaini had three children: Abubakar (the father of Ahmed Rufa’i), Dahiru Ko Tak, and Ladi Mai Goyo.

Abubakar was born in Unguwar Maude. His uncle, Hassan Sarkin Dogarai (the Head of Palace Guards) brought him up. As a young boy, Abubakar was taken to an Islamic scholar Mallam Amadu (Ahmed) in Kofar Durbi quarters of Katsina city to learn the Qur’an and acquire knowledge of Islamic jurisprudence. He apparently bonded very well with his teacher, who appreciated his character and learning and as a result gave him his daughter Ramatu (the mother of Ahmed Rufai), in marriage.

Abubakar kept on with the pursuit of Islamic education while relating with the Katsina Emirate establishment. He had by this time developed an imposing personality and appearance and because he kept a thick hairy and bold face, he was nicknamed Abu Gumuje. At the death of his paternal uncle Hassan, who never had a child, Abubakar (Abu Gumuje) who had now moved to Kano with his young family, was invited to ascend the post of Sarkin Dogarai. He politely declined the offer and returned to Kano. However, having sensed that his refusal to accept to serve as Sarkin Dogarai may have been taken for an affront by the Emirate’s establishment, Abu Gumuje, therefore, moved eastward, and ended up in Fort-Lamy, popularly known among Hausas as “Fallomi’’. In Fort-Lamy, Chad, now called Ndjamena, Malam Abu as he was popularly called, established himself as a successful merchant/transporter, and a respected cleric, as he continued with Islamic scholarship. Both Malam Abu and his spouse Ramatu died in Ndjamena where they were buried, in 1992 and 1982 respectively. Mallam Abu and Ramatu had three boys and three girls: Hajiya Halima (Amma), Dahiru, Malam Umaru Maikudi, Hajiya Fatima (all four deceased), Hajiya Rabi and Ahmed Rufai the Sardaunan Katsina and current Director General of the National Intelligence Agency (NIA). Malam Abu also had 2 boys from his Chadian wife Halima, also deceased: Ibrahim, living in Maiduguri, and Adam, living in Bangui, CAR.

Place of birth & Islamic Education

Ahmed Rufai was born in Katsina, on 11th February 1953. He grew up in Fort-Lamy where he had a sound formal basic education, first in an Arabic Primary School and thereafter a French Primary School, in addition to the education he received at home from his father and three different Quranic teachers and two other teachers of Fiqh (jurisprudence). He returned to Katsina in 1972 and lived under the guardianship of his maternal cousin Alhaji Ali K/D in Kofar Durbi, his mother’s quarters. By this time, he could speak, read and write in French and Arabic languages in addition to Hausa. Having acquired Islamic education from his father at home, coupled with his self-discipline and reserved personality, Ahmed Rufa’i was clearly ahead of his age mates in terms of knowledge, comportment, and intellectual potential. His smooth and charismatic personality immediately endeared him to earn him the respect of his peers in Kofar Durbi. He was clearly a different person because of his fine behavior, courtesy, and charisma. He was never known to have had any altercation with anybody in the neighborhood or outside. Remarkably too, he did not ignore his paternal relations at Unguwar Maude, with whom he related very well.

Formal Education

Rufai enrolled in Arabic Teachers College (ATC) Katsina, in 1974 after briefly working as a billing clerk in the Katsina District Office of Water Board, under one Mr. Emara, the District Manager. He was admitted into Bayero University, Kano through its Pre-Degree program, and graduated in 1984 with a Bachelor’s degree in French. He did his National Service at the same Bayero University where he was subsequently employed as a Graduate Assistant in the Department of English and European Languages in 1985 and rose graciously to the position of Assistant Lecturer in 1987. Combining teaching and learning, Ahmed Rufai bagged a Master’s Degree in Francophone Maghrebian Literature in 1988.

Professional Experience 

Following the Creation of Katsina State in 1987, Ahmed Rufai joined the Katsina State Civil Service in 1988, where he spent six years as head of the Political Department of the Governor’s Office. Because of his language skills, Ahmed Rufai doubled as the Secretary of the Katsina-Maradi-Zinder Tripartite Committee on the development of the border region between Katsina State in Nigeria and Maradi and Zinder Prefectures (States) in Niger Republic.

In 1993, Ahmed Rufai was spotted and recruited into the Security arm of the Nigerian Foreign Service, where, once again, he distinguished himself in good character, hard work, and devotion to duty.

After a tour of diplomatic service at the Nigeria Embassy in Morocco between 1998 and 2003, and a stint in the office of the Secretary to the Government of the Federation (SGF) in 2005, Ahmed Rufai served with distinction in the African Union (AU) and thereafter at the United Nations (UN), as political affairs officer, peacekeeper, mediator, and facilitator of peace negotiation and conflict resolution and management from January 2006 to August 2015. In this regard, he held key positions in the African Union Mission in Sudan (AMIS), the United Nations African Union Mission in Darfur (UNAMID), the United Nations Joint Support and Coordination Mechanism (JSCM) in Addis Ababa, Ethiopia, the UN Mediation Process for the Darfur conflict in Doha, Qatar, and the United Nations Office for West Africa (UNOWA) in Dakar Senegal. He also served briefly in 2015 as Senior Advisor to the Political Head of the Multinational Joint Task for Force (MNJTF) in Ndjamena, Chad. 

In November 2015, Ahmed Rufai Abubakar was appointed Senior Special Assistant to the President (SSAP) on International Relations and Foreign Affairs, bringing a solid background and wealth of experience in International Relations and Diplomacy, Security and Intelligence, Mediation, Good Governance, Peace Support Operations, as well as teaching and administration, in addition to language skills. Ahmed Rufai was not done yet as all this was crowned with his appointment, on the 9th day of January 2018 as Director General, National Intelligence Agency.

Family

Ahmed Rufai is married and is blessed with seven children. Four of them, namely Jamaal, Abdulrahman, Zinatu, and Ramatu (Ummi-Rahmat) are from his first marriage: and three others, Abubakar-Siddiq, Umar-Faruq and Zainab-Tasneem from his current spouse Fadila, 4 of 4 daughters of Ali K/D, his cousin and mentor. However, beyond this nucleus family, Rufai, a true believer in the extended family system and values, has established himself as the patriarch of the Maude descendants. He is also known for wide outreach in community support, as well as youth and women empowerment. Despite an extensive national and international public service trajectory that took him places away from Katsina and indeed Nigeria, he remained a farmer and cattle and sheep breeder in Katsina, where he has been investing in farming.

Achievements

It was in appreciation of his meritorious service career in Katsina, Nigeria, and the international system, as well as his commitment to hard work and trustworthiness that His Royal Highness, the Emir of Katsina, Alh Dr. Abdulmumini Kabir Usman, CFR, after consultation with his Council members, conferred the prestigious and legendary title of Sardaunan Katsina to Ambassador Ahmed Rufai Abubakar.

This royal gesture is applauded by the people of Katsina, Nigeria, and beyond. Ahmed Rufai Abubakar is a recipient of many awards including three DGNIA Awards for Devotion to Duty and Excellence, the National honor of Commandeur de l’Ordre National of Niger Republic conferred on him by President Mohammed Bazoum; and the National Honour of Commander of the Federal Republic, CFR conferred on him by President Muhammadu Buhari, GCFR, in 2022, among others.


اللغة العربية

سيرة شخصية

نبذة عن حياة سعادة السفري أمحد الرفاعي أبوبكر حامل لقب س ر د ون ن كتسينا واحلائز على وسام قائد اجلمهورية الفيدرالية )CFR) ينحدر سعادة السفري أمحد الرفاعي أبوبكر من نسل حممد م ودي احملارب وأمري احلرب الذائع الصيت، الذي أسس "حي مودي" مبدينة كتسنا يف الربع األخري من القرن التاسع عشر. وقد أجنب حممد م ي ستة عشر طفلا، مثاين بنات ومثانية أوالد، من بينهم التوءم ومها احلسن ود ، وهذا األخري هو ج د و احلسني أمحد الرفاعي أبوبكر )س ر د و ن ن كتسينا(. وما يعرف اليوم ابسم غ حي مودي )أ ن و ر م ودي( يف كتسينا كانت يف السابق قلعة حممد مودي ومزرعته ومنزله. وكان ا ابرزا اشتهر بلقب "ط السيد مودي حماراب ن م ر وس ا، م ي و اقا ت". وكان أيضا مرتبطاا ارتباطاا وثي بقصر أمري كتسينا و حباملي األلقاب التقليدية إبمارة كتسينا. كما كان بعض أبنائه مرتبطني ابلقصر ارتباطا ا ا كبريا مثل السيد حسن الذي خدم يف قصر أمري كتسنا بصفته رئيس حرس احلسن األخ التوءم للحسني، ج د القصر. وهذا يعىن أن ا أمحد الرفاعي، كان جزءا من النخب إال أنه مل ينجب قط، بينما أجنب أخوه احلسني ثلثة أبناء، هم: أبوبكر )والد التقليدية احلاكمة، أمحد الرفاعي(، وطاهر كوتك، والدي مي غويو. ولد أبوبكر يف حي مودي )أ نغ و ر م ودي(، حيث قام برتبيته ع مه احلسن، رئيس حرس القصر ( س ر ك ن دو غري( منذ أن كان صغريا. ومت إرسال أيب بكر إىل عامل يسمى معلم أمادو )أمحد( يف حي "قوفر دوريب" مبدينة كتسينا لتعلم القرآ الكرمي واكتساب املعرفة يف الفقة اإلسلمي. ويبدو أن املعلم أ م دو كان مرتبطاا به جدا بسبب شخصيته املهذبة وج ا ديته يف التعلم، ونتيجة لذلك زوجه ابنته اليت تسمى رامتو )رمحة(، وهي والدة أمحد الرفاعي. واصل أبوبكر سعيه وراء التعليم اإلسلمي، بينما كانت علقته جيدة مع إمارة كتسنا. وكان قد ا، وألن وجهه كان كثيف الشعر وكان أيضا جريئا، ل ا مهيبة طور وقتذاك شخصية قب أبيب ل منصب عمه، وكان وقتذاك ت دعوته لتو م غوموجي. وبوفاة عمه احلسن الذي مل ينجب قط، ت رفض العرض أبد ب قد انتقل إىل مدينة كنو للعيش هناك مع عائلته الصغرية. إال أنه ولباقة، مث رجع إىل مدينة كنو ملواصلة حياته. ولكنه أحس يف أعماقه أبن رفضه لقبول املنصب الذي عرض عليه ا رمبا يكون قد مت اعتبار ذلك إهانة من قبل اإلمارة، ولذلك توج ا ه أبو مجوج شرقا، حيث انتهى به املطاف إىل املكان الذي يطلق عليه اآلن جنامينا داخل دولة تشاد. وهناك فرض م ا مل أ بو نفسه –االسم الذي كان يطلق عليه اجلميع- ا ابعتباره تجرا وعاملا ا انجحا يف جمال وسائل النقل واملواصلت من ، وأيضا رجل دين حمرتم، إذ واصل جهوده يف العلوم الدينية. وقد تويف كل م ا مل أ ب و ور ام تو يف جنامينا، حيث مت دفنهما هناك يف عامي 1992 و1982على التوال. وكان م ا مل أ ب و ور ام تو قد أجنبا ثلثة أوالد وثلث بنات، وهم: احلاجة حليمة امللقبة ب )أ ما(، والسيد وا- رمحهم هللا-، مث احلاجة رابعة، وف طاهر، ومامل عمر ميكوطي، واحلاجة فاطمة، وكل هم قد ت والسيد أمحد الرفاعي، حامل لقب س ر د و ن ن كتسينا واملدير احلال لوكالة املخابرات الوطنية. كما كان ل " م ا مل أ بو" أيضا ولدان آخران من السيدة حليمة، زوجته التشادية واملتوفاة أيضا، ومها: إبراهيم الذي يعيش حاليا يف مدمية م غ يد ري، وآدم الذي يعيش يف ابن غي، عاصمة مجهورية أفريقيا الوسطى. ولد السيد أمحد الرفاعي يف كتسينا يف 11 فرباير 1953م. وقد نشأ وترعرع يف جنامينا، حيث درس أوال التعليم األساسي الرمسي هناك يف مدرسة ابتدائية عربية، وبعد ذلك درس أيضا يف مدرسة ابتدائية فرنسية، هذا ابإلضافة إىل التعليم الذي كان يتلقاه يف املنزل من والده ومن ثلثة معلمني للقرآن الكرمي و أيضا من معلمني آخرين للفقه. وقد عاد إىل مدينة كتسنا يف عام وف 1972م وعاش حتت رعاية ابن خالته احلاج علي )كدوان( يف حي )ق ر د ور يب( حيث كان مسكن و الدته. وكان يف ذلك الوقت إبمكانه التحدث والقراءة والكتابة ابللغات الفرنسية والعربية واهلوسا. وابإلضافة إىل حصول أمحد الرفاعي على الرتبية اإلسلمية من والده ابملنزل، وكذلك انضباطه الذايت وشخصيته املهذبة، أصبح من الواضح أنه متقدم أيضا على أقرانه من حيث العلم، والسلوك، والفكر، واإلمكاانت. فشخصيته السلسلة واجلذابة جعلته حمبواب لدى القاصي والداين، كما أكسبته احرتام أقرانه يف حي "قوف ر د ور يب". و من الواضح أيضا ا أنه كان شخصا اد ا خمتلفا بسبب حسن سلوكه، ولطفه، وجاذبيته، ومل يكن معروفا أب ا أنه كان لديه أي مشاجرة مع أي شخص داخل احلي أو خارجه. كما أنه مل يتجاهل علقاته األخرى املتعلقة جبهة أبيه يف حي م ودي ) ور مودي أ نغ ( حيث كان يرتبط هبم بشكل جيد. التحق أمحد الرفاعي بكلية معلمي اللغة العربية )ATC )بكتسينا يف عام 1974م، وذلك بعد أن عمل لفرتة وجيزة يف منصب كاتب الفواتري مبكتب مقاطعة كتسنا يف جملس املياه حتت رعاية السيد عمارة، مدير املنطقة. وبعد ذلك مت قبوله يف جامعة ابيرو، كنو، من خلل الربانمج التمهيدي، حيث خترج منها عام 1984م بدرجة البكالوريوس يف اللغة الفرنسية. وقام خبدمته الوطنية يف جامعة ابيرو نفسها، حيث مت تعيينه الحاقا أستاذا يف قسم اللغة اإلجنليزية واللغات األوروبية يف عام 1985 م وترقي إىل مرتبة "معيد" عام 1987م. وبينما مجع بني التدريس والتحصيل العلمي يف اجلامعة، استطاع السيد أمحد الرفاعي أن حيصل على درجة املاجستري يف األدب الفرنكفوين املغاريب عام 1988م. وبعد إنشاء والية كتسينا يف عام 1987م، انضم أمحد الرفاعي إىل اخلدمة املدنية لوالية كتسينا يف سنة 1988م، ا حيث أمضى ست سنوات بصفته رئيسا للدائرة السياسية يف مكتب حاكم الوالية. وبسبب مهاراته اللغوية، شغل أمحد الرفاعي منصب السكرتري للجنة كتسينا- ماراطي- زيندر الثلثية حول تنمية املنطقة احلدودية بني والية كتسينا يف نيجرياي ووالييت مراطي وزيندر يف رصد السيد أمحد الرفاعي و جتنيده يف الذراع األمنية مجهورية النيجر. ويف عام 1993م، مت للخدمة اخلارجية النيجريية، حيث تيز مرة أخرى يف حسن اخللق والعمل اجلاد والتفاين يف العمل. وبعد جولة يف السلك الدبلوماسي يف سفارة نيجرياي ابملغرب بني عام 1998م و2003م، قضى أيضا فرتة يف مكتب سكرتري احلكومة االحتادية يف عام 2005م. خدم أمحد الرفاعي أيضا ابمتيا ز يف االحتاد اإلفريقي، وبعد ذلك انتقل للعمل مع األمم املتحدة بصفته مسؤول الشؤون السياسية وحفظة السلم والوسيط وامليس ر ملفاوضات السلم وحل النزاعات وإدارهتا من يناير 2006م إىل أغسطس 2015م. ويف هذا الصدد، شغل مناصب رئيسية يف بعثة االحتاد األفريقي ابلسودان )AMIS ،)وبعثة االحتاد اإلفريقي التابعة لألمم املتحدة يف دارفور )UNAMID )و آلية الدعم والتنسيق املشرتكة لألمم املتحدة )JSCM )يف أديس أاباب، إبيثوبيا، وعملية وساطة األمم املتحدة لنزاع دارفور ابلدوحة، قطر، ومكتب األمم املتحدة لغرب أفريقيا )UNOWA )يف داكار ابلسنغال. كما عمل لفرتة وجيزة بصفته املستشار األول للرئيس السياسي لقوة املهام املشرتكة متعددة اجلنسيات )MNJTF )يف جنامينا، بتشاد. ، مت تعيني السيد أمحد الرفاعي أبوبكر املساعد األول اخلاص للرئيس ويف نوفمرب 2015م )SSAP )للعلقات الدولية والشؤون اخلارجية ، وذلك لتوفره على أسس معرفية ي قوة وثروة هائلة من اخلربة يف العلقات الدولية، والدبلوماسية، واألمن، واالستخبارات، والوساطة، واحلكم الرشيد، وعمليات دعم السلم، وكذلك التدريس، واإلدارة، ابإلضافة إىل املهارات اللغوية. ومل يقف األمر عند هذا احل د، بل تتوي مت ج جمهوداته السابقة يف 9 من يناير 2018، حيث مت تعيينه املدير العام لوكالة املخابرات الوطنية. إن سعادة السيد أمحد الرفاعي قد تزوج و رزق بسبعة أطفال، أربعة منهم من زواجه األول، وهم: مجال، وعبد الرمحن، وزينة، ورمحة. وثلثة آخرون هم: أبوبكر الصديق، وعمر الفارو ق، وزينب تسنيم، وهم من السيدة فضيلة زوجته احلالية، وابنة احلاج علي )كدوان( ابن خالته ومرشده. وجبانب عائلته الصغرية فإن السيد أمحد الرفاعي مؤمن حىت النخاع بنظام األسرة املمتدة وقيمها، ب حيث أثبت نفسه على أ جلميع أ نه أ حفاد مودي. وهو معروف أيضا بدعمه للمجتمع على نطاق واسع، وكذلك تكني الشباب واملرأة. ا وعلى الرغم من مسار خدمته العامة على املستوى الوطين والدول الذي أخذه بعيدا عن مسقط رأسه ا كتسينا ونيجرياي بصفة عامة، فقد ظل مزارعا ومربيا للماشية واألغنام يف كتسنا، حيث ما زال يستثمر يف الزراعة هناك. ا وتقديرا ملسريته املهنية اجلديرة ابلتقدير يف كتسنا ونيجرياي والنظام الدول، وكذلك التزامه ابلعمل اجلاد واجلدير ابلثقة، وبعد تشاور الدكتور عبد املؤمن كبري عثمان، صاحب السمو امللكي أمري كتسنا مع أعضاء جملسه، قرر صاحب السمو منح اللقب املرموق واألسطوري الذي هو س ر د و ن ن كتسنا لسعادة السفري أمحد الرفاعي أبوبكر، وذلك من أجل التنويه و اإلشادة به. وقد لقيت هذه اللفتة امللكية حفاوة ابلغة من قبل شعب كتسنا و من داخل نيجرياي وخارجها. وجتدر اإلشارة يف هذا املقام إىل أن السيد أمحد الرفاعي أبوبكر كان قد حصل على عدة جوائز، مبا يف ذلك ثلث جوائز للمدير العام لوكالة املخابرات الوطنية تنويها بتفانيه يف أداء الواجب ا و التميز، وكذلك الوسام الوطين لقائد القوات املسلحة الوطنية من مجهورية النيجر الذي منحه إايه فخامة الرئيس حممد ابزوم، مث الوسام الوطين لقائد اجلمهورية الفيدرالية املمنوح له من قبل فخامة الرئيس حممد هباري، يف عام 2022م، والو سام الوطين للستحقاق من قبل فخامة الرئيس عمر سيسوكو إمبالو، رئيس مجهورية غينيا بيساو، وغريها من اجلوائز. ديسمرب 2022م


Harshen Hausa

Takaitaccen Tarihin Sardaunan Katsina, Jakada Ahmed Rufai Abubakar, CFR

Jakada Ahmed Rufai Abubakar dan tsatson sanannen jarumin nan ne, Muhammad Maude, wanda ya kafa Unguwar Maude da ke cikin Birnin Katsina tun a wajen zangon karshe na karni na 19. Allah ya albarkaci Muhammad Maude da ‘ya’ya 16: takwas mata, takwas maza. Daga cikin ‘ya’ya mazan akwai tagwaye; Hassan da Hussaini. Toh Hussainin shi ne kakan Jakada Ahmed Rufai. Muhammad Maude, a wancan lokacin, shi ke mulkin Unguwar da a yanzu ake kira Unguwar Maude a cikin Birnin Katsina, kuma a nan ne gidan sa da gonakin sa suke. Jaruntakar Maude ta kai har ana yi masa lakabi da Dan Marusa, Mai Wuta. Abinda ya kara kusantar da shi ga Masarautar Katsina da manyan mutanen Fada. Haka ma, wasu daga cikin ‘ya’yan sa. Alal misali, Hassan wanda shi ne abokin tagwaicin Hussaini, wato kakan Ahmed Rufai Abubakar, ya kasance a matsayin Sarkin Dogarai wanda hakan ya sa ya yi aminci tare da daukacin Masarautar sosai. Shi dai Sarkin Dogarai Hassan Allah bai ba shi haihuwa ba amma abokin tagwaicin sa Hussaini, Allah ya albarkace shi da ‘ya’ya guda ukku da suka hada da Abubakar (mahaifin Ahmed Rufai) da Dahiru Ko Tak da Ladi Mai Goyo. An haifi Abubakar a Unguwar Maude, kuma ya taso karkashin kulawar abokin tagwaicin baban sa wato Sarkin Dogarai Hassan, wanda kuma shi ne ya sanya shi a Makarantar Malam Amadu da ke Kofar Durbi a cikin Birnin Katsina domin yin Karatun Alkur’ani da Ilimin addinin Musulunci. Saboda irin maida hankali da kwazo da Abubakar ya nuna ga karatu ya sanya Malamin sa wato Malam Amadu ya aura masa da diyar sa Ramatu, wato mahaifiyar Ahmed Rufai. Abubakar ya ci gaba da neman Ilimin addinin Musulunci Kuma ga shi yana da kyakkyawar alaka da Masarauta. Haka nan kuma, ya kasance mutum ne mai kwarjini da cika fuska, ga kuma gemu da ya tsaida; wanda hakan ya sa ake masa lakani da Abu Gumuje. Bayan rasuwar Hassan Sarkin Dogarai, sai Masarautar Katsina ta nemi Abubakar da ya zo ya gaji wannan Sarauta ta Sarkin Dogarai; kasancewar shi Hassan bai taba haihuwa ba. Shi kuwa Abubakar a lokacin shi da iyalin sa sun koma da zama a Kano, sai ya ba da hakuri tare da nuna rashin amincewa ya karbi wannan sarautar. Daga bisani sai Abu Gumuje ya ga kamar rashin karbar sarautar nan da bai yi ba ya yi wa masarautar Katsina zafi, don haka sai ya bar garin Kano ya nutsa Gabas inda ya sami kansa a garin Fort-Lamy wanda aka fi sani da Fallomi ta Kasar Chadi, wanda a halin yanzu ake kira Birnin Ndjamena. Malam Abu, kamar yadda aka fi sanin sa a Kasar, ya sami karbuwa a garin Fallomi ta fuskar Kasuwanci da Safara; bugu da kari kuma Malami ne da ake girmama shi domin kuwa ya ci gaba da al’amurran sa na neman ilmin addinin Musulunci. Mahaifiyar Ahmed Rufai, wato Ramatu, ta rasu a shekarar 1982, yayin da kuma ya rasa mahaifin sa Malam Abu a shekarar 1992, Allah ya jikan su da rahamar Sa. Dukkan su sun rasu a garin Ndjamena. Malam Abu da Mahaifiyar Ahmed Rufai sun haifi ‘ya’ya shidda; uku maza, uku mata da suka hada da Hajiya Halima wadda ake kira Amma, da Dahiru da Malam Umaru Maikudi da Hajiya Fatima; wadanda su ma tuni suka rasu, sai kuma Hajiya Rabi da shi Ahmed Rufai wato Sardaunan Katsina kuma Babban Daraktar Hukumar Ayyukan Sirri ta Kasar nan. Malam Abu yana kuma da wasu ‘ya’ya guda biyu, Ibrahim da Adam wadanda matar da ya aura a Kasar Chadi mai suna Halima ta haifa masa. Ita ma wannan matar, tuni ta riga mu gidan gaskiya. A halin da ake ciki kuma, shi Ibrahim yana nan a Maiduguri, yayin da shi kuma Adam yake zaune a Birnin Bangui na Jamhuriyar Africa ta Tsakiya. An haifi Ahmed Rufai Abubakar a Katsina ranar 11 ga watan Feburairu na shekarar 1953 Miladiyya. Ya taso a garin Fort Lamy; kuma a nan ne ya fara karatun sa na firamare inda da farko ya fara yin Makarantar Firamare ta harshen Larabci, sannan kuma ya koma ya yi Makarantar Firamare ta harshen Faransanci. Haka nan, ya yi karatun Alkur’ani a wajen mahaifin sa Malam Abu da wasu Malaman Kur’ani guda Ukku, sa’annan kuma ya yi karatun Ilimin Fiqhu a wajen wasu Malamai guda biyu. Ahmed ya dawo Katsina a shekarar 1972 inda ya zauna a karkashin kulawar dan babar sa Alhaji Ali K/D a Unguwar Kofar Durbi cikin Birnin Katsina, watau Unguwar da aka haifi Mahaifiyar sa. A wannan lokaci ya kasance ya iya magana da karatu da rubutu da Harsunan Larabci da Faransanci da kuma Hausa. Ilimi da Tarbiyar da Ahmed Rufai ya samu daga wajen Iyayen sa, ya sa ya kasance mutumin kirki kuma kamili wanda hakan ya sa ya yi wa abokan sa da sa’o’in sa zarra ta fannin Ilimi da natsuwa da kuma basira wajen gudanar da al’amuran su na yau da kullum. Har ila yau, Ahmed Rufai Abubakar ya kasance mai kwarjini wanda hakan ya sa abokan sa da sa’o’in sa ke girmama shi. Wadannan Kyawawan dabi’u sun sa ya bambanta a cikin su domin kuwa ba a taba ganin ya yi fada da wani ba a cikin Unguwar Kofar Durbi da makobtan ta. Wani abun burgewa ga Ahmed Rufai Abubakar shi ne, duk da kasancewar yana zaune tare da dangin mahaifiyar sa ne bai sa shi ya yada zumunci da bangaren dangin mahaifin sa dake a Unguwar Maude ba domin kuwa yana da kyakkyawar alaka da su. Ahmed Rufai ya yi karatun sa na Sakandare a Makarantar Horas da Malaman Larabci ta Katsina. Bayan da ya kammala a shekarar 1974 ya yi aiki na wani dan lokaci a Ofishin Hukumar Samar da Ruwa da ke Shiyyar Katsina a karkashin Manajan Shiyyar mai suna Mr. Emera. Daga bisani, ya sami damar shiga Jami’ar Bayero da ke Kano a bangaren karatun share fagen shiga Jami’a; daga nan ya zarce da karatun sa na Digiri na farko a fannin nazarin Harshen Faransanci. Yayi aikin Hidimar Kasa a cikin Jami’ar. Bayan da ya kammala, sai Jami’ar Bayeron ta dauke shi aiki a matsayin Karamin Malamin Jami’a a Sashen Nazarin Turanci da Harsunan Kasashen Turawa a shekarar 1985 in da ya kai har ga matakin Malamin Jami’a a shekarar 1987. Yana cikin wannan aiki na koyarwar ne kuma, ya yi karatun sa na Digiri na Biyu a shekarar 1988 a fannin Adabin Kasashen Larabawa da ke karkashin Mulkin Kasar Faransa. Bayan da aka kirkiro Jihar Katsina a shekarar 1987, Ahmed Rufai Abubakar ya koma da aiki karkashin Gwamnatin Jihar Katsina a shekarar 1988 a inda ya shafe shekaru shidda yana shugabantar Sashen al’amurran Siyasa a Ofishin Gwamna. Saboda kwarewar sa a magana da harsuna daban-daban ya sa Ahmed Rufai ya rike mukamin Sakataren Kwamitin Hadaka na Cigaban Iyakokin Jihohin Katsina da Maradi da Zinder dake a Nijeriya da Jamhuriyar Nijar da kuma Kwamitin Iyakokin Jihohin Maradi da Zinder da ke a Jamhuriyar Nijar. Lura da aka yi da aiki tukuru da kuma hazakar da Ahmed Rufai ke nunawa a wajen gudanar da aiki, ya sa aka dauke shi aiki a karkashin Gwamnatin Tarayya a Bangaren Hukumar Ayyukan Sirri ta Kasa a Kasashen Waje; inda a can ma ya ba mara da kunya ta hanyar jajircewa da aiki tukuru. Ambasada Ahmed (Rufai) ya yi aikin diflomasiyya a ofishin Jakadancin Nijeriya da ke Kasar Morocco tsakanin shekarar 1998 da 2003. Daga nan kuma ya yi aiki a Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya a shekarar 2005. Haka kuma, hazakar sa ta kara bayyana karara a lokacin da ya yi aiki da Kungiyar Kasashen Afirika da kuma a karkashin Majalisar Dinkin Duniya daga watan Janairu na shekarar 2006 zuwa watan Augusta na shekarar 2015 a matsayin Jami’in da ke kula da Harkokin Siyasa da Tabbatar da Zaman Lafiya da Sasanci da Shiga tsakani don daidaita al’amurra domin a samu zaman lafiya tsakanin yankunan da ke fama da rikice-rikice. A tsakanin wannan lokacin, Ahmed Rufai ya rike mukamai da dama a ayyuka daban-daban da aka aiwatar da suka hada da aikin diflomasiyya da aka gudanar a Kasar Sudan a karkashin Kungiyar Kasashen Afirika (AMIS) da aikin hadin guiwa da aka gudanar tsakanin Majalisar Dinkin Duniya da Kungiyar Kasashen Afirika a yankin Darfur (UNAMID) da kuma aikin hadin guiwa na bada tallafi na Majalisar Dinkin Duniya da aka gudanar a Addis Ababa da ke kasar Habasha (JSCM) da aikin Sasanci akan rikicin yankin Darfur da Majalisar Dinkin Duniya ta gudanar a birnin Doha na kasar Qatar da kuma lokacin da yake aiki a ofishin Majalisar Dinkin Duniya na Yammacin Afirika dake Birnin Dakar na kasar Senegal (UNOWA). Har ila yau, Ahmed Rufai Abubakar ya yi aiki na wani dan lokaci a shekarar 2015 a matsayin Babban Mai ba da Shawara ga Shugaban Sashen Al’amurran Siyasa na Kwamitin Gamo da Kasawa na hadin guiwar Kasashe daban-daban da aka gudanar a Ndjamena, Babban Birnin Kasar Chadi (MNJTF). Likkafa ta kara gaba a watan Nuwamba na shekarar 2015, lokacin da aka nada Ahmed Rufai Abubakar a matsayin Babban Mai taimaka wa Shugaban Kasa akan dangantakar Kasa da Kasa da harkokin Kasashen Waje (SSAP); inda ya ba da gudunmuwa ta amfani da kwarewar sa a fagen al’amurran da suka shafi dangantakar Kasashe da Diflomasiyya da harkokin tsaro na sirri da sasanci da kyakkyawan shugabancin da ayyukan da suka shafi tabbatar da zaman lafiya da koyarwa da harkokin mulki da kuma baiwar da Allah ya ba shi ta Magana da harsuna dabandaban. Ambasada Ahmed bai tsaya a nan ba domin kuwa a ranar 9 ga watan Janairu na Shekarar 2018 Allah ya dada wa daben sa makuba, saboda kwarewar sa da aiki tukuru da kishin kasa aka nada Ahmed Rufai Abubakar a matsayin Babban Daraktan Hukumar Ayyukan Sirri ta Kasa, wato NIA, wanda Shugaban Kasa Muhammadu Buhari, GCFR ya tabbatar masa. Ahmed Rufai Abubakar yana da mata da kuma ‘ya’ya bakwai, hudu daga cikin su Jamal da Abdulrahman da Zinatu da kuma Ramatu wadanda matar sa ta farko ta haifa; yayin da sauran guda ukun: Abubakar Sadiq da Umar Faruk da Zainab-Tasmeem, mai dakin sa ta yanzu, Fadila, diyar dan babar sa Ali K/D ta haife su. Ahmed Rufai Abubakar mutum ne mai son dangi, don haka ya tsaya tsayin daka tamkar uba ga zuriyar Maude. Ya kuma kasance mai son ci gaban al’umma da kuma ba da tallafi ga Matasa da Mata domin ci gaban rayuwar su da tattalin arzikin su. Duk da irin dawainiyar aiki da yake yi a cikin Nijeriya da Kasashen Waje; wanda hakan ya sa yakan kasance nesa da Katsina da ma Nijeriyar kanta, bai sa ya fasa Noma da Kiwon dabbobi a Katsina ba. Domin yabawa da irin wannan gudunmuwa da aiki tukuru da sadaukar da kai ga cigaban Jihar Katsina da Nijeriya da kuma harkokin Kasa da Kasa, Mai Martaba Sarkin Katsina Alhaji (Dr.) Abdulmuminu Kabir Usman, CFR ya ba Ahmed Rufai Abubakar Babbar Sarauta ta Sardaunan Katsina bayan tuntubar Manyan ‘Yan Majalisar sa. Ba shi wannan Sarauta karramawa ce ga Al’ummar Jihar Katsina da Nijeriya har ma da Kasashen Ketare. Ahmed Rufai Abubakar ya sami lambobin yabo da dama wadanda suka hada da Lambar Yabo ta Babban Darektan Hukumar Ayyukan Sirri ta Kasa (NIA) har karo ukku da Lambar Yabo ta Babban Kwamanda na Jamhuriyar Nijar wadda Shugaban Kasa Mohammed Bazoum ya ba shi, da kuma Lambar Yabo ta Nijeriya ta CFR wadda Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya ba shi a wannan shekarar ta 2022, da kuma Lambar Yabo da Shugaban Kasar Guinea Bisau Umaru Cissoko Embalsoya ba shi da dai sauransu. Disamba, 2022